Makaɗan Hausa A Gombe: Tasirin Makaɗan Fada A Masarautar Buba Yero

    Tsakure

    Hausawa mutane ne da aka san su da shiga lungu-lungu da saƙo-saƙo na yankunan maƙwabtansu na kusa da na nesa. Mutane ne da ke da sha’awar tafiye-tafiye don neman kyakkyawar matsuguni na samun ɗan abin tasarrufi na sa wa a bakin salati. A duk inda suka ya da zango sukan yi wa al’ummar da suka taras tasiri da harshensu da al’adunsu. Wannan takarda ta yi nazarin makaɗa da mawaƙan fada waɗanda suka kwararo jihar Gombe kuma suke rayuwa suna nishaxantar da masarautar ta Fulani da kaɗe-kadensu da waƙoƙinsu na fasaha da bushe-bushensu. An kuma kawo dalilai da suka haifar da zuwan Huasawa ƙasar Gombe da sabubban cuɗanyarsu da Fulani a Gombe. Takardar ta yi amfani da hanyar hira da masu ba da bayanai da kuma ajiyayyun takardu don tattara bayanai da suka taimaka wajen taskace nau’o’in makaɗa da mawaƙan Hausa da suke masarautar. Daga ciki, an kawo makaɗan taushi da na turu da na kotso da na ganga da na ruwa da kuma masu bushe-bushe. An yi bayanin waɗanda suka assasa kowane kiɗa a masarautar da inda suka fito da waɗanda suka gaje su, da kuma lokutan da suka fi gabatar da waƙoƙin nasu. Binciken ya gano akwai makaɗan Hausa maza da mata a fadar masarautar da suka shafi dukkan rukuni na mawaƙan da aka gabatar a nan sama. An kuma kawo ‘yan misalai na wasu ɗiyan waƙoƙin makaɗan. Binciken ya nuna yadda ‘ya’ya da jikoki da aka haifa a masarautar suka taimaka wajen gina al’ummar nan da aka fi sani da Hausa/Fulani wato narkewar al’adun al’ummu guda biyu waje ɗaya.

    Kalmomin Fannu: Makaɗa, Mawaƙa, Tasiri, Gombe, Fada
    DOI:  www.doi.org/10.36349/tjllc.2023.v02i01.017

    author/Ibrahim Lamido, Ph.D & Bashir Garba

    journal/Tasambo JLLC | 15 May 2023 |  P. 138-144

    pdf-https://drive.google.com/file/d/1E61B6lNgSMLGdukVy4d6gbj8Y3YxOTAi/view?usp=share_link

    paper-https://drive.google.com/file/d/1E61B6lNgSMLGdukVy4d6gbj8Y3YxOTAi/view?usp=share_link