‘Yan Ta’adda a Kalmomin ‘Yan Jarida a Jihar Zamfara

    Tsakure

    Sadarwa wata hanya ce ta isar da saƙo ko bayanai daga wani zuwa wani. Saboda haka sadarwa yanayin sarrafa bayanai ne tsakanin alumma cikin tsari da hikima. A wannan takarda an yi tsokaci a kan rawar da ‘yan jarida ke takawa wajen fito da sunayen ‘Yan ta’adda musamman a jihar Zamfara inda ayyukansu ya fi shafuwa. Manufa a nan ita ce, tabbatar da wanzuwar kalmomin da ‘yan jarida ke amfani da su a yayin yayata ayyukan masu ta’addanci da faɗakarwa a kafafen watsa labarai kama daga rediyo da talabijin har zuwa ga kafafen sada zumunta irin su intanet WhatsApp da facebook da ire-irensu. Bugu da ƙari, dubarun da aka yi amfani da su wajen gudanar da wannan bincike sun haɗa da; zantawa da ‘yan jaridu na kafafen watsa labarai daban-daban da suka haɗa da; gidan talabijin na ƙasa da ke Gusau (NTA Gusau) da gidan rediyo da talabijin na jihar Zamfara da rediyon FM na ƙasa da ke jihar Zamfara da gidan talabijin na Gamji Gusau da gidan rediyon BBC Hausa da ke London. Sakamakon binciken da aka fito da su sun haɗa da; samar da wannan nau’in Hausa na da nasaba da faɗakarwa ga mutane da ire-iren sunayen da ake kiran wannan rukunin mutane domin ankara daga sharrinsu.

    Fitilun Kalmomi: Ta’addanci, ‘Yan Ta’adda, ‘Yan Jarida, Zamfara

    DOI:  www.doi.org/10.36349/tjllc.2023.v02i01.020

    author/Abbas, N.I. & Sarkin Fada, I.

    journal/Tasambo JLLC | 15 May 2023 |  P. 162-167

    pdf-https://drive.google.com/file/d/1vfQlgNOun0ouIE_shWyZLhbE3UjIYJzD/view?usp=sharing

    paper-https://drive.google.com/file/d/1vfQlgNOun0ouIE_shWyZLhbE3UjIYJzD/view?usp=sharing