Tasirin Musulunci a Kan Auren Hausawa

    Tsakure

    Rarrabe tsakanin al’adun aure da Hausawa suka gada kaka da kakanni da abubuwan da addinin Musulunci ya ya zo da su, ba abu ne mai sauÆ™i ba. Idan aka lura da irin tasirin da addinin Musulunci ya yi a kusan dukkan É“angarorin rayuwa, za a ga cewa wasu abubuwa da suka shafi aure sun sauya daga abin da al’ada ta zo da shi ya zuwa ga abin da addinin Musulunci ya zo da shi. Musulunci ya zo da dukkan tsare-tsare, kuma rashin bin wannan tsari na Musulunci, kan iya zama barazana ga auren ma’aurata da kuma rayuwarsu ta gaba É—aya. Wannan takarda  na da manufar: bayyana auren Hausawa, ta kuma fito da tasirin Musulunci a kan auren Hausawa tare da haskaka alfanun Musuluncin a cikin auren Hausawa. Hanyar da aka bi wajen aiwatar da wannan bincike ta haÉ—a da hira da wasu mutane da karance-karancen littattafai da kundayen binjcike. An É—ora wannan maÆ™alar a kan ra’in Sauyin al’adu. MaÆ™alar,  ta fito da irin tasirin da Musulunci ya yi a wasu al’adun Hausawa na aure, tun daga kore wasu, sauya wasu, da kuma samar da wasu al’adun.

    Keywords: Al’ada, aure, Musulunci da tasiri

     DOI: www.doi.org/10.36349/tjllc.2024.v03i01.026

    author/Maikwari, H.U. & Lawan, M.S.

    journal/Tasambo JLLC | 15 February 2024 |  Article 26