Tsakure
Sunan wannan takarda shi ne “Maguɗin Zaɓe a Tarihin Siyasar Jam’iyyu a Arewacin Nijeriya: Nazari daga Rubutaccen Zuben Hausa”. A cikin wannan
takarda an duba yadda maguɗin zaɓe ya ginu a cikin tarihin
siyasa Arewacin Nijeriya. Manufar wannan
bincike shi ne yin nazarin maguɗin zaɓe a cikin tarihin
siyasar jam’iyyu daga ayyukan rubutaccen zube. Takardar ta mayar da hankali ne ga
siyasar Arewacin Nijeriya, domin ganin yadda maguɗin zaɓe ya ginu a cikinta. Hanyoyin da aka yi
amfani da su wajen tattara bayanan da wannan nazarin ya yi amfani da su sun haɗa da: Karance-karance na ayyukan da aka samu a kan siyasa musamman waɗanda suka shafi maguɗin zaɓe, inda aka samu bayanan da suka taimaka wajen gina
wannan maƙalar. An duba
jaridu da jawaban siyasa da wasiƙu da kuma ƙagaggun labarai waɗanda suke ɗauke da ruhin siyasar jam’iyyu a cikinsu domin samun batutuwan da aka kafa hujja da su. An yi amfani da ra’in Tarihanci wanda aka ɗora binciken a kansa. A ƙarshe takardar ta gano cewa maguɗin zaɓe abu ne da ya ginu a
cikin siyasar jam’iyyu tun daga farkonta, kuma har yanzu ana amfani da shi
domin fafutukar neman ɗarewa bisa madafun iko a cikin siyasar Arewacin Nijeriya.
Fitilun Kalmomi: Maguɗi, Zaɓe, Tarihi, Siyasa,
Maguɗin Zaɓe
DOI: www.doi.org/10.36349/tjllc.2025.v04i01.001
author/Sarkin Gulbi, A., Ahmad, U., Karofi, U.A., Rambo, R.A. & Sani, A-U.
journal/Tasambo JLLC 4(1) | September 2024 |