Maguɗin Zaɓe a Tarihin Siyasar Jam’iyyu a Arewacin Nijeriya: Nazari Daga Rubutaccen Zuben Hausa

    Tsakure

    Sunan wannan takarda shi ne “Maguɗin Zaɓe a Tarihin Siyasar Jam’iyyu a Arewacin Nijeriya: Nazari daga Rubutaccen Zuben Hausa”. A cikin wannan takarda an duba yadda maguɗin zaɓe ya ginu a cikin tarihin siyasa Arewacin Nijeriya. Manufar wannan bincike shi ne yin nazarin maguɗin zaɓe a cikin tarihin siyasar jam’iyyu daga ayyukan rubutaccen zube. Takardar ta mayar da hankali ne ga siyasar Arewacin Nijeriya, domin ganin yadda maguɗin zaɓe ya ginu a cikinta. Hanyoyin da aka yi amfani da su wajen tattara bayanan da wannan nazarin ya yi amfani da su sun haɗa da: Karance-karance na ayyukan da aka samu a kan siyasa musamman waɗanda suka shafi maguɗin zaɓe, inda aka samu bayanan da suka taimaka wajen gina wannan maƙalar. An duba jaridu da jawaban siyasa da wasiƙu da kuma ƙagaggun labarai waɗanda suke ɗauke da ruhin siyasar jamiyyu a cikinsu domin samun batutuwan da aka kafa hujja da su. An yi amfani da ra’in Tarihanci wanda aka ɗora binciken a kansa. A ƙarshe takardar ta gano cewa maguɗin zaɓe abu ne da ya ginu a cikin siyasar jam’iyyu tun daga farkonta, kuma har yanzu ana amfani da shi domin fafutukar neman ɗarewa bisa madafun iko a cikin siyasar Arewacin Nijeriya.

    Fitilun Kalmomi: Maguɗi, Zaɓe, Tarihi, Siyasa, Maguɗin Zaɓe

    DOI: www.doi.org/10.36349/tjllc.2025.v04i01.001

    author/Sarkin Gulbi, A., Ahmad, U., Karofi, U.A., Rambo, R.A. & Sani, A-U.

    journal/Tasambo JLLC 4(1) | September 2024 |