Alƙur’ani Malamin Mallammai Shaihin Da Shaihuna Ka Roƙo Fatawa

    Tsakure: Saukar Alƙur’ani na farko ya zo shekarar (610 CE), ya ƙare shekarar (622CE). Alƙur’ani an saukar da shi ga Annabi Muhammadu (SAW) ta hanyar Mala’ika Jibril. Da kalmar “Iqra” aka fara magana. Littafi ne da ke da Surori (114) da aka kasa zuwa hizifi (60). Ayoyi 6,666, kalmomi 157,935 da harufan da suka gina su 668,684; Allah Ka buwaya. Asalin harufan harshen Larabci (28) ne. Daga cikinsu akwai harufu 15 marasa masu ɗigogi, guda 13 kuma masu ɗigogi. Harufa 7 ke da ɗigo ɗaya, 3 ɗigo biyu, 2 ɗigo uku. Manyan wasula su ne “Alu Baƙi" da “Alu Ja” sai “wasulan sama da ƙasa” da “damma da shadda”. Waɗannan suke ba da damar karanta alƙur’ani ga kowa. A fassara Alƙur’ani cikin harsuna 114. A harsuna 47 kawai aka samu wallafa shi cikakke. A fagen masana, an yi tafsiran Alƙur’ani 2,700, amma 300 kawai aka samu wallafawa. A cikin harsunan Nijeriya kimanin 500, an fassara Alƙur’ani cikin fitattun harsuna cikin rubutun bokon harshe, da ajamin harshe. Daga cikinsu akwai: Hausa, Yoruba, Kanuri, Fulfulde, Nupe, Kyanganci da Igbo. A tarihance, Indiya ta fara taron gasar karatun addinai fiye da shekara 100 da suka gabata, shekarar da aka gayyato Musulmi shi ne ya zama zakara. Ta karatun Alƙur’ani an fara ta a Indonesia a shekarar 1940, sai Malaysia (1961), Saudiya ta fara a 1980. A zamanin da muke ciki (2024), Nijeriya ce gaba da yawan mahardata Alƙur’ani wanda Daular Borno ke jagoranta. Harshen da ya fi harsunan Nijeriya ga fassara Alƙur’ani shi ne Hausa. A Najeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo ta fara tsara shi a Kabi a matsayin karo na 39. Akwai buƙatar saka Alƙur’ani cikin tsarin koyarwa daga Firamare zuwa Jami’a, a ƙara fassara Alƙur’ani cikin Harsunan Nijeriya domin tsaro da kyautata shugabanci.

    Fitilun Kalmomi: Alƙur’ani, Musulunci, Ƙasar Hausa, Hausawa

    DOI: www.doi.org/10.36349/tjllc.2025.v04i01.005

    author/Aliyu Muhammadu Bunza

    journal/Tasambo JLLC 4(1) | May 2025 |