Tasirin Karin Harshen ‘Yan Gudun Hijira a Kan Hausar Garin Ƙauran Namoda, Jihar Zamfara

    Tsakure: 

    A ’yan shekarun nan, matsalar tsaro a wasu sassan Arewa maso Yammacin Nijeriya ta haifar da yawaitar ’yan gudun hijira zuwa garuruwa daban-daban waɗanda suke zaune lafiya kamar a cikin garin Ƙauran Namoda. Wannan hijira ta zo da sauye-sauye masu yawa, ciki har da na zamantakewa da tattalin arziƙi da kuma harshe. Wannan bincike ya nazarci tasirin karin harshen ’yan gudun hijira, musamman waɗanda suka taso daga yankunan ƙasar Shinkafi (Arewacin garin Ƙauran Namoda) da kuma waɗanda suka fito daga yankin ƙasar Zurmi (Arewa Maso-Gabas da garin Ƙauran Namoda) da kuma wani yanki na ƙasar Birnin Magaji (Gabas da garin Ƙauran Namoda). Sai kuma na wasu ƙauyuka da ke kudancin garin na Ƙauran Namoda duk a cikin jihar Zamfara, inda suka shigo da wannan baƙon karin harshe zuwa garin Ƙauran Namoda, a yayin da suke neman mafaka don gudun tsira daga matsalar rashin tsaro da suka fuskanta a muhallansu na asali. Hakan, ya yi matuƙar shafar wasu kalmomi ta fuskar ma’ana, musamman waɗanda ake amfani da su a Hausar garin ta asali wadda aka san su da ita, watau Karin harshen Zamfarci, inda ake samun canjin ma’ana . An tattara bayanai ta hanyar gani da ido, an yi tattaunawa da mazauna gari da ’yan gudun hijira, tare da yin amfani da littattafan masana. Sakamakon binciken ya nuna cewa, karin harshen ’yan gudun hijira yana da tasiri mai kyau da kuma ƙalubale ga harshen Hausar Kauran Namoda. Binciken ya bayar da shawarwari a kan yadda za a ci gajiyar wannan sauyi ba tare da gurɓata harshen asali ba (Zamfarci), wanda ɗaya ne daga cikin kare-karen harsunan ƙasar Hausa.

    Fitilun Kalmomi: Harshe, Karin Harshe, Walwalar Harshe, Gudun Hijira, Kauran Namoda

    DOI: www.doi.org/10.36349/tjllc.2026.v05i02.005

    author/Abdullahi Bashir & Mustapha Abubakar 

    journal/Tasambo JLLC 5(2) | February 2026 |